Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 8:19-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

19. Da na gutsuttsura wa mutum dubu biyar gurasan nan biyar, kwando nawa kuka ɗauka cike da gutsattsarin?” Suka ce masa, “Sha biyu.”

20. “To, gurasa bakwai da na gutsuttsura wa mutum dubu huɗu fa? Manyan kwanduna nawa kuka ɗauka cike da gutsattsarin?” Suka ce masa, “Bakwai.”

21. Sai ya ce musu, “To, har yanzu ba ku fahimta ba?”

22. Suka iso Betsaida. Aka kawo masa wani makaho, aka roƙe shi ya taɓa shi.

Karanta cikakken babi Mar 8