Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 8:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A lokacin nan da wani taro mai yawan gaske ya sāke haɗuwa, ba su kuwa da abinci, sai ya kira almajiransa, ya ce musu,

2. “Ina jin tausayin wannan taro, don yau kwanansu uku ke nan a guna, ba su da wani abinci.

3. In kuwa na sallame su su tafi gida da yunwa haka, ai, za su kasa a hanya, ga shi kuwa, waɗansunsu sun fito nesa.”

4. Sai almajiransa suka amsa masa suka ce, “Ina za a iya samun gurasar da za ta ciyar da mutanen nan a jeji haka?”

5. Sai ya tambaye su, “Gurasa nawa gare ku?” Suka ce, “Bakwai.”

6. Sai ya umarci taron su zauna a ƙasa. Da ya ɗauki gurasan nan bakwai, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya yi ta ba almajiransa su kai wa taron, suka kuwa kakkai musu.

7. Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan. Da ya yi wa Allah godiya, sai ya ce su ma a kai musu.

Karanta cikakken babi Mar 8