Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 7:1-10 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. To, da Farisiyawa suka taru a wurinsa tare da waɗansu daga cikin malaman Attaura da suka zo daga Urushalima,

2. suka lura waɗansu almajiransa na cin abinci da hannuwa marasa tsarki, wato marasa wanki.

3. Domin Farisiyawa da dukan Yahudawa ba sa cin abinci sai sun wanke hannu sarai tukuna, saboda bin al'adun shugabanninsu.

4. In sun komo daga kasuwa kuwa, ba sa cin abinci sai sun yi wanka tukuna. Akwai kuma waɗansu al'adu da yawa da suka gada suke kiyayewa, kamar su wankin ƙore, da tuluna, da daruna.

5. Sai Farisiyawa da malaman Attaura suka tambaye shi, “Don me almajiranka ba sa bin al'adun shugabanni, sai su riƙa cin abinci da hannuwa marasa tsarki?”

6. Sai ya ce musu, “Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku, munafukai! Yadda yake a rubuce cewa,‘Al'umman nan a baka kawai suke girmama ni,Amma a zuci nesa suke da ni.

7. A banza suke bauta mini,Domin ƙa'idodin da suke koyarwa umarnin ɗan adam ne.’

8. Kuna yar da umarnin Allah, kuna riƙe da al'adun mutane.”

9. Sai ya ce musu, “Lalle kun iya yar da umarnin Allah don ku bi al'adunku!

10. Domin Musa ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ da kuma, ‘Wanda ya zagi ubansa ko uwa tasa, sai lalle a kashe shi.’

Karanta cikakken babi Mar 7