Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 5:1-7 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Suka iso hayin teku a ƙasar Garasinawa.

2. Da saukarsa daga jirgin, sai ga wani mai baƙin aljan daga makabarta ya tarye shi.

3. Shi kuwa makabarta ce mazauninsa. Ba mai iya ɗaure shi kuma, ko da sarƙa ma.

4. Don dā an sha ɗaure shi da mari da sarƙa, amma ya tsintsinka sarƙar, ya gutsuntsuna marin, har ma ba mai iya bi da shi.

5. Kullum kuwa dare da rana yana cikin makabarta, da kan duwatsu, yana ta ihu, yana kukkuje jikinsa da duwatsu.

6. Da dai ya hango Yesu, sai ya sheƙo a guje ya fāɗi a gabansa,

7. ya ƙwala ihu ya ce, “Ina ruwanka da ni, Yesu Ɗan Allah Maɗaukaki? Na gama ka da Allah, kada ka yi mini azaba.”

Karanta cikakken babi Mar 5