Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 4:38-41 Littafi Mai Tsarki (HAU)

38. Yesu kuwa na daga ƙarshen baya na jirgin a kan matashi, yana barci. Sai suka tashe shi, suka ce masa, “Malam, za mu hallaka ba ka kula ba ko?”

39. Sai ya farka, ya tsawata wa iskar, ya kuma ce wa ruwan tekun, “Natsu! Ka yi shiru!” Sai iskar ta kwanta, wurin duk ya yi tsit.

40. Ya ce musu, “Don me kuka firgita haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?”

41. Sai suka tsorata, matuƙar tsoro, suka ce wa juna, “Wa ke nan kuma, wanda har iska da ruwan teku ma suke yi masa biyayya?”

Karanta cikakken babi Mar 4