Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 3:29-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. amma fa, duk wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki ba ya samun gafara har abada, ya yi madawwamin zunubi ke nan.”

30. Wannan kuwa don sun ce, “Yana da baƙin aljan ne.”

31. Sa'an nan uwa tasa da 'yan'uwansa suka zo. Suna tsaye a waje, sai suka aika masa yă je.

32. Taro kuwa na zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Ga tsohuwarka da 'yan'uwanka suna nemanka a waje.”

33. Ya amsa musu ya ce, “Su wane ne tsohuwata da 'yan'uwana?”

34. Sai ya waiwayi waɗanda suke zaune kewaye da shi, ya ce, “Ga tsohuwata a nan da 'yan'uwana!

35. Ai, kowa ya yi abin da Allah yake so, shi ne ɗan'uwana, ita ce 'yar'uwata, ita ce kuma tsohuwata.”

Karanta cikakken babi Mar 3