Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 3:10-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. saboda ya riga ya warkar da mutane da yawa, har ya kai ga duk masu cuta na dannowa wurinsa domin su taɓa shi.

11. Baƙaƙen aljannu kuwa, duk sa'ad da suka gan shi, sai su fāɗi gabansa suna kururuwa, suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne.”

12. Sai ya kwaɓe su ƙwarai kada su bayyana shi.

13. Ya hau dutse, ya kira waɗanda yake so, suka je wurinsa.

14. Ya zaɓi mutum goma sha biyu su zauna tare da shi, ya riƙa aikensu suna wa'azi.

Karanta cikakken babi Mar 3