Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 3:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. Sai ya sāke shiga majami'a. Akwai wani mutum a nan kuwa mai shanyayyen hannu.

2. Sai suka yi haƙwansa su ga ko zai warkar da shi ran Asabar, don su samu su kai ƙararsa.

3. Sai ya ce wa mai shanyayyen hannun, “Fito nan fili.”

4. Ya ce musu, “Ya halatta ran Asabar a yi alheri ko kuwa mugunta? A ceci rai, ko kuwa a kashe shi?” Amma sai suka yi shiru.

5. Da ya duddube su da fushi, yana baƙin ciki da taurin zuciyarsu, sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye.

Karanta cikakken babi Mar 3