Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 2:25-28 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. Sai ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba, sa'ad da ya matsu da yunwa, shi da abokan tafiyarsa?

26. Yadda ya shiga masujadar Allah a zamanin Abiyata babban firist, ya ci keɓaɓɓiyar gurasan nan, wadda bai halatta kowa ya ci ba, sai firistoci kaɗai, har ma ya ba abokan tafiyarsa?”

27. Sai ya ce musu, “Ai, Asabar domin mutum aka yi ta, ba mutum aka yi domin Asabar ba.

28. Saboda haka Ɗan Mutum shi ne Ubangijin har da na ranar Asabar ma.”

Karanta cikakken babi Mar 2