Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 2:2-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Aka kuwa taru maƙil har ba sauran wuri, ko a bakin ƙofa. Shi kuwa yana yi musu wa'azin Maganar Allah.

3. Sai suka kawo masa wani shanyayye, mutum huɗu suna ɗauke da shi.

4. Da suka kāsa kusatarsa don yawan mutane, suka buɗe rufin soron ta sama da shi. Da suka huda ƙofa kuwa, suka zura gadon da shanyayye yake kwance a kai.

5. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, an gafarta maka zunubanka.”

6. To, waɗansu malaman Attaura na nan zaune, suna ta wuswasi a zuciya tasu,

7. suna cewa, “Don me mutumin nan yake faɗar haka? Ai, sāɓo yake! Wa yake da ikon gafarta zunubi banda Allah kaɗai?”

8. Nan da nan, da Yesu ya gane a ransa suna ta wuswasi haka a zuci, sai ya ce musu, “Don me kuke wuswasi haka a zuciyarku?

9. Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta maka zunubanka’, ko kuwa a ce, ‘Tashi ka ɗauki shimfiɗarka ka yi tafiya’?

10. Amma don ku sakankance Ɗan Mutum na da ikon gafarta zunubi a duniya”–sai ya ce wa shanyayyen–

11. “Na ce maka, tashi ka ɗauki shimfiɗarka ka tafi gida.”

Karanta cikakken babi Mar 2