1. Bayan 'yan kwanaki, da ya sāke komowa Kafarnahum, sai aka ji labari yana gida.
2. Aka kuwa taru maƙil har ba sauran wuri, ko a bakin ƙofa. Shi kuwa yana yi musu wa'azin Maganar Allah.
3. Sai suka kawo masa wani shanyayye, mutum huɗu suna ɗauke da shi.