27. Suka kuma gicciye 'yan fashi biyu tare da shi, ɗaya dama da shi, ɗaya kuma a hagun. [
28. Wannan shi ne cikar Nassin nan da ya ce, “An lasafta shi a cikin masu laifi.”]
29. Masu wucewa suka yi ta yi masa baƙar magana, suna kaɗa kai, suna cewa, “Ahaf! kai da za ka rushe Haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku,
30. to, sauko daga gicciyen, ka ceci kanka mana!”