Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 15:23-30 Littafi Mai Tsarki (HAU)

23. Suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, amma ya ƙi sha.

24. Sa'an nan suka gicciye shi, suka rarraba tufafinsa a junansu, suna kuri'a a kansu, su ga abin da kowa zai samu.

25. Da ƙarfe tara na safe suka gicciye shi.

26. Aka kuma rubuta sanarwar laifinsa sama da shi, wato “Sarkin Yahudawa.”

27. Suka kuma gicciye 'yan fashi biyu tare da shi, ɗaya dama da shi, ɗaya kuma a hagun. [

28. Wannan shi ne cikar Nassin nan da ya ce, “An lasafta shi a cikin masu laifi.”]

29. Masu wucewa suka yi ta yi masa baƙar magana, suna kaɗa kai, suna cewa, “Ahaf! kai da za ka rushe Haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku,

30. to, sauko daga gicciyen, ka ceci kanka mana!”

Karanta cikakken babi Mar 15