Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 14:59-66 Littafi Mai Tsarki (HAU)

59. Duk da haka dai shaida tasu ba ta zo ɗaya ba.

60. Sai babban firist ya miƙe a tsakiyarsu ya tambayi Yesu ya ce, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”

61. Amma yana shiru abinsa, bai amsa kome ba. Sai babban firist ɗin ya sāke tambayarsa, “To, ashe, kai ɗin nan ne Almasihu Ɗan Maɗaukaki?”

62. Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum zaune dama ga Mai Iko, yana kuma zuwa cikin gajimare.”

63. Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa, ya ce, “Wace shaida kuma za mu nema?

64. Kun dai ji saɓon da ya yi! Me kuka gani?” Duk suka yanke masa shari'a a kan ya cancanci kisa.

65. Waɗansu ma suka fara tattofa masa yau, suka ɗaure masa idanu, suka bubbuge shi, suna ce masa, “Yi annabci!” Dogaran Haikali kuma suka yi ta marinsa.

66. Bitrus kuwa na ƙasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo.

Karanta cikakken babi Mar 14