Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 14:51-62 Littafi Mai Tsarki (HAU)

51. Sai wani saurayi, daga shi sai mayafi, ya bi shi. Suka kai masa cafka,

52. shi kuwa ya bar musu mayafin, ya gudu huntu.

53. Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. Duk manyan firistoci da shugabanni da malaman Attaura suka taru a wurinsa.

54. Bitrus kuma ya bi shi daga nesa nesa, har cikin gidan babban firist ɗin, ya zauna cikin dogaran Haikali, yana jin wuta.

55. To, manyan firistoci da 'yan majalisa duka suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi, amma ba su samu ba.

56. Da yawa kam, sun yi masa shaidar zur, amma bakinsu bai zo ɗaya ba.

57. Daga baya kuma waɗansu suka taso, suka yi masa shaidar zur suka ce,

58. “Mun ji ya ce, wai zai rushe Haikalin nan da mutane suka gina, ya gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba.”

59. Duk da haka dai shaida tasu ba ta zo ɗaya ba.

60. Sai babban firist ya miƙe a tsakiyarsu ya tambayi Yesu ya ce, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?”

61. Amma yana shiru abinsa, bai amsa kome ba. Sai babban firist ɗin ya sāke tambayarsa, “To, ashe, kai ɗin nan ne Almasihu Ɗan Maɗaukaki?”

62. Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum zaune dama ga Mai Iko, yana kuma zuwa cikin gajimare.”

Karanta cikakken babi Mar 14