Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 14:38-43 Littafi Mai Tsarki (HAU)

38. Ku zauna a faɗake, ku yi addu'a kada ku faɗa ga gwaji. Lalle ruhu ya ɗauka, amma jiki rarrauna ne.”

39. Sai ya sāke komawa, ya yi addu'a, yana maimaita maganar dā.

40. Har wa yau kuma ya sāke dawowa, ya samu suna barci, don duk barci ya cika musu ido ƙwarai, sun kuwa rasa abin da za su ce masa.

41. Ya sāke komowa zuwa na uku, ya ce musu, “Har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka. Lokaci ya yi. An ba da Ɗan Mutum ga masu zunubi.

42. Ku tashi mu tafi. Kun ga, ga mai bashe ni ɗin nan ya matso!”

43. Nan da nan, kafin ya rufe baki sai ga Yahuza, ɗaya daga cikin sha biyun nan, da taron mutane riƙe da takuba da kulake, manyan firistoci, da malaman Attaura, da shugabanni ne suka turosu.

Karanta cikakken babi Mar 14