24. Sa'an nan ya ce musu, “Wannan jinina ne na tabbatar da alkawari, wanda za a bayar saboda mutane da yawa.
25. Hakika, ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabi ba, sai dai a ranan nan da zan sha wani sabo a Mulkin Allah.”
26. Da suka yi waƙar yabon Allah, sai suka fita suka tafi Dutsen Zaitun.