Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 12:13-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

13. Suka aiko masa da waɗansu Farisiyawa da mutanen Hirudus, don su burma shi cikin magana tasa.

14. Da suka zo, suka ce masa, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, ba ka kuma zaɓen kowa, domin ka ɗauki kowa da kowa daidai, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa?

15. Mu biya, ko kada mu biya?” Shi kuwa da ya gane makircinsu, ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku kawo mini dinari in gani.”

16. Suka kawo masa. Ya ce musu, “Suran nan da sunan nan na wane ne?” Suka ce masa, “Na Kaisar ne.”

Karanta cikakken babi Mar 12