Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 10:3-16 Littafi Mai Tsarki (HAU)

3. Sai ya amsa musu ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”

4. Suka ce, “Musa ya ba da izini a rubuta takardar kisan aure, a kuma saki matar.”

5. Yesu ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya rubuta muku wannan umarni.

6. Amma tun farkon halitta ‘Allah ya halicce su, namiji da tamata.’

7. ‘Don haka fa sai mutum yă bar uwa tasa da ubansa, yă manne wa mata tasa.

8. Haka su biyun nan su zama jiki guda.’ Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne.

9. Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.”

10. A cikin gida kuma sai almajiransa suka sāke tambayarsa wannan magana.

11. Sai ya ce musu, “Kowa ya saki mata tasa, ya auri wata, zina yake yi da ta biyun.

12. In kuma matar ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”

13. Suna kawo masa waɗansu yara ƙanana domin ya taɓa su, sai almajiransa suka kwaɓe su.

14. Da Yesu ya ga haka, sai ya ji haushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai, Mulkin Allah na irinsu ne.

15. Hakika, ina gaya muku, duk wanda bai yi na'am da Mulkin Allah kamar yadda ƙaramin yaro yake yi ba, ba zai shiga Mulkin ba har abada.”

16. Sai Yesu ya rugume su, yana ɗora musu hannu, yana sa musu albarka.

Karanta cikakken babi Mar 10