Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 10:15-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Hakika, ina gaya muku, duk wanda bai yi na'am da Mulkin Allah kamar yadda ƙaramin yaro yake yi ba, ba zai shiga Mulkin ba har abada.”

16. Sai Yesu ya rugume su, yana ɗora musu hannu, yana sa musu albarka.

17. Ya fara tafiya ke nan, sai ga wani ya sheƙo a guje, ya durƙusa a gabansa, ya tambaye shi ya ce, “Malam managarci, me zan yi in gaji rai madawwami?”

18. Sai Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Ai, ba wani Managarci sai Allah kaɗai.

19. Ka dai san umarnan nan, ‘Kada ka yi kisankai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi shaidar zur. Kada ka yi zamba. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’ ”

20. Sai ya ce masa, “Malam, ai, duk na kiyaye waɗannan tun ƙuruciyata.”

Karanta cikakken babi Mar 10