Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Mar 1:31-43 Littafi Mai Tsarki (HAU)

31. Sai ya matso, ya kama hannunta, ya tashe ta, zazzaɓin kuwa ya sake ta, har ta yi musu hidima.

32. Da magariba, bayan faɗuwar rana, aka kakkawo masa dukan marasa lafiya, da masu aljannu.

33. Sai duk garin ya haɗu a ƙofar gidan.

34. Ya warkar da marasa lafiya da yawa, masu cuta iri iri, ya kuma fitar wa mutane aljannu da yawa. Bai ko yarda aljannun su yi wata magana ba, domin sun san shi.

35. Da asussuba ya tashi ya fita, ya tafi wani wuri inda ba kowa, ya yi addu'a a can.

36. Sai Bitrus da waɗanda suke tare da shi suka bi shi.

37. Da suka same shi, suka ce masa, “Duk ana nemanka.”

38. Ya ce musu, “Mu tafi garuruwan da suke gaba, in yi wa'azi a can kuma, domin saboda haka ne na fito.”

39. Ya gama ƙasar Galili duk yana wa'azi a majami'unsu, yana kuma fitar wa mutane aljannu.

40. Wani kuturu ya zo wurinsa, yana roƙonsa, yana durƙusawa a gabansa, yana cewa, “In ka yarda kana da iko ka tsarkake ni.”

41. Da tausayi ya kama Yesu, sai ya miƙa hannu, ya taɓa shi, ya ce masa, “Na yarda, ka tsarkaka.”

42. Nan take sai kuturtar ta rabu da shi, ya tsarkaka.

43. Ya kwaɓe shi ƙwarai, ya sallame shi nan da nan,

Karanta cikakken babi Mar 1