Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 9:51-55 Littafi Mai Tsarki (HAU)

51. Da lokacin karɓarsa a Sama ya gabato, ya himmantu sosai ga zuwa Urushalima.

52. Sai ya aiki jakadu su riga shi gaba, suka kuwa tafi suka shiga wani ƙauyen Samariyawa su shisshirya masa.

53. Amma Samariyawa suka ƙi karɓarsa, domin niyyarsa duk a kan Urushalima take.

54. Da almajiransa Yakubu da Yahaya suka ga haka suka ce, “Ya Ubangiji, ko kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama ta lashe su?”

55. Amma ya juya, ya tsawata musu.

Karanta cikakken babi Luk 9