Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 7:30-38 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. Amma Farisiyawa da masanan Attaura suka shure abin da Allah yake nufinsu da shi, da yake sun ƙi ya yi musu baftisma.

31. “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Waɗanne iri ne su?

32. Kamar yara suke da suke zaune a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,‘Mun busa muku sarewa, ba ku yi rawa ba,Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.’

33. Ga shi, Yahaya Maibaftisma ya zo, ba ya cin gurasa, ba ya shan ruwan inabi, amma kuna cewa, ‘Ai, yana da iska.’

34. Ga Ɗan Mutum ya zo, yana ci yana sha, kuna kuma cewa, ‘Ga mai haɗama, mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi!’

35. Duk da haka hikimar Allah, ta dukkan aikinta ne ake tabbatar da gaskiya tata.”

36. Wani Bafarisiye ya kira shi cin abinci. Sai ya shiga gidan Bafarisiyen, ya ƙishingiɗa wurin cin abincin.

37. Sai ga wata matar garin, mai zunubi, da ta ji Yesu na cin abinci a gidan Bafarisiyen, ta kawo wani ɗan tandu na man ƙanshi,

38. ta tsaya a bayansa a wajen ƙafafunsa, tana kuka. Sai hawayenta ya fara zuba a ƙafafunsa, ta goge su da gashinta, ta yi ta sumbantarsu, ta shafa musu man ƙanshin.

Karanta cikakken babi Luk 7