Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 7:29-33 Littafi Mai Tsarki (HAU)

29. Da duk jama'a da masu karɓar haraji suka ji haka, suka tabbata Allah mai adalci ne, aka yi musu baftisma da baftismar Yahaya.

30. Amma Farisiyawa da masanan Attaura suka shure abin da Allah yake nufinsu da shi, da yake sun ƙi ya yi musu baftisma.

31. “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Waɗanne iri ne su?

32. Kamar yara suke da suke zaune a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,‘Mun busa muku sarewa, ba ku yi rawa ba,Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.’

33. Ga shi, Yahaya Maibaftisma ya zo, ba ya cin gurasa, ba ya shan ruwan inabi, amma kuna cewa, ‘Ai, yana da iska.’

Karanta cikakken babi Luk 7