Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 7:25-35 Littafi Mai Tsarki (HAU)

25. To, kallon me kuka je yi? Wani mai adon alharini? Ai kuwa, masu adon gaske, masu zaman annashuwa, a fāda suke.

26. To, kallon me kuka je yi? Annabi? Hakika, ina gaya muku, har ya fi annabi nesa.

27. Wannan shi ne wanda labarinsa yake rubuce cewa,‘Ga shi, na aiko manzona ya riga ka gaba,Wanda zai shirya maka hanya gabaninka.’

28. Ina gaya muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.”

29. Da duk jama'a da masu karɓar haraji suka ji haka, suka tabbata Allah mai adalci ne, aka yi musu baftisma da baftismar Yahaya.

30. Amma Farisiyawa da masanan Attaura suka shure abin da Allah yake nufinsu da shi, da yake sun ƙi ya yi musu baftisma.

31. “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Waɗanne iri ne su?

32. Kamar yara suke da suke zaune a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,‘Mun busa muku sarewa, ba ku yi rawa ba,Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.’

33. Ga shi, Yahaya Maibaftisma ya zo, ba ya cin gurasa, ba ya shan ruwan inabi, amma kuna cewa, ‘Ai, yana da iska.’

34. Ga Ɗan Mutum ya zo, yana ci yana sha, kuna kuma cewa, ‘Ga mai haɗama, mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi!’

35. Duk da haka hikimar Allah, ta dukkan aikinta ne ake tabbatar da gaskiya tata.”

Karanta cikakken babi Luk 7