Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 7:15-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuwa ya ba da shi ga uwa tasa.

16. Sai tsoro ya kama su duka, suka ɗaukaka Allah suna cewa, “Lalle, wani annabi mai girma ya bayyana a cikinmu,” da kuma, “Allah ya kula da jama'arsa.”

17. Wannan labarin nasa kuwa ya bazu a dukan ƙasar Yahudiya da kewayenta.

18. Sai almajiran Yahaya suka gaya masa dukan abubuwan nan.

Karanta cikakken babi Luk 7