Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 6:24-31 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. “Amma kaitonku, ku masu arziki domin kun riga kun sami taku ta'aziyya.

25. “Kaitonku, ku da kuke ƙosassu a yanzu, don za ku ji yunwa. “Kaitonku, ku masu dariya a yanzu, don za ku yi baƙin ciki, ku yi kuka.

26. “Kaitonku in kowa na yabonku. Haka kakanninsu ma suka yi wa annabawan ƙarya.”

27. “Amma ina gaya muku, ku masu sauraro, ku ƙaunaci magabtanku, ku yi wa maƙiyanku alheri.

28. Ku sa wa masu zaginku albarka. Masu wulakanta ku kuma, ku yi musu addu'a.

29. Wanda ya mare ka a kunci ɗaya, juya masa ɗaya kuncin kuma. Wanda ya ƙwace maka mayafi, kada ka hana masa taguwarka ma.

30. Duk wanda ya roƙe ka, ka ba shi. Wanda kuma ya ƙwace maka kaya, kada ka neme shi.

31. Yadda kuke so mutane su yi muku, to, ku yi musu haka.

Karanta cikakken babi Luk 6