Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 4:8-17 Littafi Mai Tsarki (HAU)

8. Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake cewa,‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada,Shi kaɗai za ka bauta wa.’ ”

9. Sai kuma ya kai shi Urushalima, ya ɗora shi can kan tsororuwar Haikali, ya ce masa, “In dai kai Ɗan Allah ne, to, dira ƙasa daga nan,

10. don a rubuce yake cewa,‘Zai yi wa mala'ikunsa umarni game da kai, su kiyaye ka,’

11. da kuma‘Za su tallafe ka,Don kada ka yi tuntuɓe da dutse.’ ”

12. Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Ai kuwa an ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’ ”

13. Bayan da Iblis ya gama irin dukan gwaje-gwajensa, ya rabu da shi ɗan lokaci tukuna.

14. Yesu ya koma ƙasar Galili, ikon Ruhu yana tare da shi. Labarinsa ya bazu a dukan kewayen.

15. Ya yi ta koyarwa a majami'unsu, duk ana girmama shi.

16. Ya zo Nazarat inda aka rene shi. Ya shiga majami'a a ran Asabar kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe domin ya yi karatu.

17. Aka miƙa masa Littafin Annabi Ishaya, ya buɗe littafin, ya sami inda aka rubuta cewa,

Karanta cikakken babi Luk 4