Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 4:15-21 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Ya yi ta koyarwa a majami'unsu, duk ana girmama shi.

16. Ya zo Nazarat inda aka rene shi. Ya shiga majami'a a ran Asabar kamar yadda ya saba. Sai ya miƙe domin ya yi karatu.

17. Aka miƙa masa Littafin Annabi Ishaya, ya buɗe littafin, ya sami inda aka rubuta cewa,

18. “Ruhun Ubangiji yana tare da ni,Domin yā shafe ni in yi wa matalauta bishara.Ya aiko ni in yi shelar saki ga ɗaurarru,In kuma buɗe wa makafi ido,In kuma 'yanta waɗanda suke a danne,

19. In yi shelar zamanin samun karɓuwa ga Ubangiji.”

20. Ya rufe littafin ya mayar wa mai hidima, ya zauna. Duk waɗanda suke cikin majami'a suka zuba masa ido.

21. Sai ya fara ce musu, “Yau Nassin nan ya cika a kunnenku.”

Karanta cikakken babi Luk 4