2. a zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, Maganar Allah ta zaike wa Yahaya ɗan Zakariya a jeji.
3. Sai ya zaga duk lardin bakin Kogin Urdun, yana wa'azi, cewa mutane su tuba a yi musu baftisma, domin a gafarta musu zunubansu,
4. yadda yake a rubuce a Littafin Annabi Ishaya cewa,“Muryar mai kira a jeji tana cewa,Ku shirya wa Ubangiji tafarki,Ku miƙe hanyoyinsa,
5. Za a cike kowane kwari,Kowane dutse da kowane tsauni za a baje su.Za a miƙe karkatattun wurare,Za a bi da hanyoyin da ba su biyu ba.