Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 24:31-39 Littafi Mai Tsarki (HAU)

31. Idonsu ya buɗe, suka kuma gane shi. Sai ya ɓace musu.

32. Suka ce wa juna, “Ashe, zuciyarmu ba ta yi annuri ba, sa'ad da yake a hanya, yana bayyana mana Littattafai?”

33. Anan take, suka tashi suka koma Urushalima, suka sami sha ɗayan nan tare gu ɗaya, da kuma waɗanda suke tare da su,

34. suna cewa, “Hakika Ubangiji ya tashi, har ya bayyana ga Bitrus!”

35. Su kuma suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane shi a wajen gutsura gurasa.

36. Suna cikin faɗar waɗannan abubuwa, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu, ya ce musu, “Salama alaikun!”

37. Amma suka firgita, tsoro ya kama su, suka zaci fatalwa suke gani.

38. Sai ya ce musu, “Don me kuka firgita, kuke kuma tantama a zuciyarku?

39. Ku dubi hannuwana da ƙafafuna, ai, ni ne da kaina. Ku taɓa ni, ku ji, don fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”

Karanta cikakken babi Luk 24