Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 23:10-18 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Manyan firistoci da malaman Attaura na nan a tsaitsaye, suna tsananta kai ƙararrakinsa ainun.

11. Sai Hirudus da sojansa suka wulakanta shi, suka yi masa ba'a, da suka sa masa tufafi masu ƙawa kuma, suka mai da shi wurin Bilatus.

12. A ran nan sai Hirudus da Bilatus suka yi sulhu, don dā abokan gāba ne.

13. Bilatus ya tara manyan firistoci da shugabanni da kuma jama'a,

14. ya ce masu, “Kun kawo mini mutumin nan a kan, wai yana ɓad da jama'a, na kuwa tuhunce shi a gabanku, amma ban same shi da wani laifi a ƙararrakinsa da kuka kawo ba.

15. Hirudus ma bai samu ba, don ya komo mana da shi. Ga shi kuwa, bai yi wani abu da ya cancanci kisa ba.

16. Saboda haka, zan yi masa bulala in sake shi.”[

17. A lokacin idi kuwa lalle ne ya sakar musu ɗaurarre guda.]

18. Amma duk suka ɗauki ihu gaba ɗaya, suna cewa, “A yi da wannan ɗin, a sakar mana Barabbas!”

Karanta cikakken babi Luk 23