Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 2:1-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

1. A kwanakin nan Kaisar Augustas ya yi shela, cewa a rubuta dukkan mutanen da suke ƙarƙashin mulkinsa.

2. Wannan shi ne ƙirga na fari da aka yi a zamanin Kiriniyas, mai mulkin ƙasar Suriya.

3. Kowa sai ya tafi garinsu a rubuta shi.

4. Yusufu shi ma ya tashi daga birnin Nazarat, a ƙasar Galili, ya tafi ƙasar Yahudiya, ya je birnin Dawuda, da ake kira Baitalami (domin shi daga gidan Dawuda ne, na cikin zuriyarsa),

5. don a rubuta shi, duk da Maryamu tashinsa, wadda take kuma da ciki.

Karanta cikakken babi Luk 2