Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 14:15-19 Littafi Mai Tsarki (HAU)

15. Da jin haka, sai ɗaya daga cikin abokan cinsa ya ce masa, “Albarka tā tabbata ga wanda zai ci abinci a Mulkin Allah.”

16. Amma ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa.

17. Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa yă ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, duk an shirya kome,’

18. Sai dukansu baki ɗaya suka fara kawo hanzari. Na farko ya ce masa, ‘Na sayi gona, lalle ne in je in gano ta. Ina roƙonka ka ɗauke mini,’

19. Sai wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma, za ni in gwada su. Ina roƙonka ka ɗauke mini.’

Karanta cikakken babi Luk 14