Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 12:39-43 Littafi Mai Tsarki (HAU)

39. Amma dai ku sani, da maigida zai san lokacin da ɓarawo zai zo, da ya zauna a faɗake, ya hana a shiga masa gida.

40. Ku ma sai ku zauna a kan shiri, domin a lokacin da ba ku zata ba Ɗan Mutum zai zo.”

41. Sai Bitrus ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa na kowa da kowa ne?”

42. Ubangiji ya ce, “Wane ne amintaccen wakilin nan mai hikima, da ubangidansa zai ba shi riƙon gidansa, yă riƙa ba su abincinsu a kan kari?

43. Albarka tā tabbata ga bawan da, in ubangidansa ya dawo, zai samu yana yin haka.

Karanta cikakken babi Luk 12