7. Amma ba su da ɗa, don Alisabatu bakararriya ce, dukansu biyu kuma sun tsufa.
8. Ana nan, wata rana Zakariya na kan hidima tasa ta firist, a sa'ad da hidimar ta kewayo kan ƙungiyarsu,
9. bisa ga al'adar hidimar firistoci, sai kuri'a ta nuna shi ne mai shiga Haikalin Ubangiji, ya ƙona turare.
10. A lokacin ƙona turare kuwa duk taron jama'a suna waje, suna addu'a,
11. sai wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, yana tsaye a dama da bagadin ƙona turare.