Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:7-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. Amma ba su da ɗa, don Alisabatu bakararriya ce, dukansu biyu kuma sun tsufa.

8. Ana nan, wata rana Zakariya na kan hidima tasa ta firist, a sa'ad da hidimar ta kewayo kan ƙungiyarsu,

9. bisa ga al'adar hidimar firistoci, sai kuri'a ta nuna shi ne mai shiga Haikalin Ubangiji, ya ƙona turare.

10. A lokacin ƙona turare kuwa duk taron jama'a suna waje, suna addu'a,

11. sai wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, yana tsaye a dama da bagadin ƙona turare.

Karanta cikakken babi Luk 1