Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:68-73 Littafi Mai Tsarki (HAU)

68. “Ubangiji Allahn Isra'ila,A gare shi ne lalle yabo yake tabbata,Domin ya kula, ya yi wa jama'a tasa fansa.

69. Ya ta da Mai Ceto mai iko dominmu,Daga zuriyar baransa Dawuda.

70. Yadda tuntuni ya faɗa ta bakunanAnnabawa nasa tsarkakan nan,

71. Yă cece mu daga abokan gābanmu,Har ma daga dukan maƙiyanmu.

72. Domin nuna jinƙai ne ga kakanninmu,Ya tuna da alkawarinsa mai tsarkin nan.

73. Shi ne rantsuwan nan wadda ya yi wa ubanmu Ibrahim,

Karanta cikakken babi Luk 1