Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Luk 1:30-34 Littafi Mai Tsarki (HAU)

30. Mala'ikan kuma ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.

31. Ga shi kuma, za ki yi ciki, ki haifi ɗa, ki kuma sa masa suna Yesu.

32. Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki.Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dawuda,

33. Zai kuma mallaki zuriyar Yakubu har abada,Mulkinsa kuwa ba shi da matuƙa.”

34. Sai Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Ƙaƙa wannan zai yiwu, tun da yake ba a kai ni ɗaki ba?”

Karanta cikakken babi Luk 1