Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Kol 4:2-5 Littafi Mai Tsarki (HAU)

2. Ku lazamci yin addu'a, kuna zaune a faɗake a kanta sosai, tare da gode wa Allah,

3. mu ma ku yi mana addu'a Allah ya buɗe mana hanyar yin Maganarsa, mu sanar da asirin Almasihu, wanda saboda shi ne nake a ɗaure,

4. domin in bayyana shi sosai, kamar yadda ya kamata in faɗa.

5. Ku tafiyar da al'amuranku da hikima a cikin zamanku tare da marasa bi, kuna matuƙar amfani da lokaci.

Karanta cikakken babi Kol 4