Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Gal 4:5-11 Littafi Mai Tsarki (HAU)

5. domin ya fanso waɗanda suke a ƙarƙashin Shari'a, a mai da mu a matsayin 'ya'yan Allah.

6. Tun da yake ku 'ya'ya ne, sai Allah ya aiko da Ruhun Ɗansa a cikin zukatanmu, yana kira, “Ya Abba! Uba!”

7. Don haka, kai ba bawa ba ne kuma, amma ɗa ne. Da yake ɗa ne kuma, to, magāji ne bisa ga ikon Allah.

8. Dā da ba ku san Allah ba, kuna bauta wa waɗansu gumaka, waɗanda ga ainihi ba a bakin kome suke ba.

9. Amma a yanzu da kuka san Allah, ko ma dai a ce Allah ya san ku, ta yaya za ku sāke komawa a kan raunanan al'adu marasa biyan bukata, har kuna neman komawa ga bautarsu?

10. Ga shi, al'adun ranaku, da na watanni, da na lokatai, da na shekaru ba sa wuce ku!

11. Amma kun ba ni tsoro, kada ya zamana na yi wahala a kanku a banza!

Karanta cikakken babi Gal 4