Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

Filib 2:16-22 Littafi Mai Tsarki (HAU)

16. kuna riƙe da maganar rai kankan, har a ranar bayyanar Almasihu in yi taƙama, cewa himmata da famana ba a banza suke ba.

17. Ko da za a tsiyaye jinina a kan hadaya da hidima na bangaskiyarku, sai in yi farin ciki, in kuma taya ku farin ciki, ku duka.

18. Haka ku ma, ya kamata ku yi farin ciki, ku kuma taya ni farin ciki.

19. Ina sa zuciya ga Ubangiji Yesu in aika muku da Timoti da wuri, don ni ma in ƙarfafa da samun labarinku.

20. Ba ni da wani kamarsa, wanda da sahihanci zai tsananta kula da zamanku lafiya.

21. Dukansu sha'anin gabansu kawai suke yi, ba na Yesu Almasihu ba.

22. Amma, ai, kun san darajar Timoti yadda muka yi bautar bishara tare, kamar ɗa da mahaifinsa.

Karanta cikakken babi Filib 2