Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 8:24-29 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Sai saminu ya amsa ya ce, “Ku roƙar mini Ubangiji kada ko ɗaya daga cikin abin da kuka faɗa ya aukar mini.”

25. To, bayan manzannin sun tabbatar da Maganar Ubangiji, sun faɗe ta, suka koma Urushalima, suna yin bishara a ƙauyukan Samariyawa da yawa.

26. Sai wani mala'ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Tashi, ka yi kudu, ka bi hanyar da ta fito daga Urushalima zuwa Gaza,” wato hanyar hamada.

27. Sai ya tashi ya tafi. Ga wani mutumin Habasha, wani bābā, mai babban matsayi a mulkin Kandakatu, sarauniyar Habasha, shi ne kuwa ma'ajinta, ya zo Urushalima ne yin sujada,

28. yana komawa gida a zaune a cikin keken dokinsa, yana karatun littafin Annabi Ishaya.

29. Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa ka yi kusa da keken dokin nan.”

Karanta cikakken babi A.m. 8