Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 8:21-26 Littafi Mai Tsarki (HAU)

21. Ba ruwanka da wannan al'amari sam, don zuciyarka ba ɗaya take ba a gaban Allah.

22. Saboda haka sai ka tuba da wannan mugun aiki naka, ka roƙi Ubangiji ko a gafarta maka abin da ka riya a zuciyarka.

23. Domin na ga kai tushen ɗaci ne, kana kulle a cikin mugunta.”

24. Sai saminu ya amsa ya ce, “Ku roƙar mini Ubangiji kada ko ɗaya daga cikin abin da kuka faɗa ya aukar mini.”

25. To, bayan manzannin sun tabbatar da Maganar Ubangiji, sun faɗe ta, suka koma Urushalima, suna yin bishara a ƙauyukan Samariyawa da yawa.

26. Sai wani mala'ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Tashi, ka yi kudu, ka bi hanyar da ta fito daga Urushalima zuwa Gaza,” wato hanyar hamada.

Karanta cikakken babi A.m. 8