Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 8:11-20 Littafi Mai Tsarki (HAU)

11. Sai suka mai da hankali gare shi, don ya daɗe yana ta ba su al'ajabi da sihirinsa.

12. Amma da suka gaskata bisharar da Filibus ya yi a kan Mulkin Allah, da kuma sunan Yesu Almasihu, duka aka yi musu baftisma mata da maza.

13. Har Saminu da kansa ma ya ba da gaskiya, bayan an yi masa baftisma kuma ya manne wa Filibus. Ganin kuma ana yin mu'ujizai da manyan al'ajibai, ya yi mamaki ƙwarai.

14. To, da manzannin da suke Urushalima suka ji Samariyawa sun yi na'am da Maganar Allah, suka aika musu da Bitrus da Yahaya.

15. Su kuwa da suka iso, suka yi musu addu'a don su sami Ruhu Mai Tsarki,

16. domin bai sauko wa ko wannensu ba tukuna, sai dai kawai an yi musu baftisma ne da sunan Ubangiji Yesu.

17. Sai suka ɗora musu hannu, suka kuwa sami Ruhu Mai Tsarki.

18. To, da Saminu ya ga, ashe, ta ɗora hannun manzanni ne ake ba da Ruhun, sai ya miƙa musu kuɗi,

19. ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iko, don kowa na ɗora wa hannu, yă sami Ruhu Mai Tsarki.”

20. Amma Bitrus ya ce masa, “Ku hallaka, kai da kuɗinka, don ka zaci da kuɗi ne za ka sami baiwar Allah!

Karanta cikakken babi A.m. 8