Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 8:10-13 Littafi Mai Tsarki (HAU)

10. Duk jama'a kuwa suka mai da hankali a gare shi, babba da yaro, suna cewa, “Mutumin nan, ai, ikon nan ne na Allah, da ake kira mai girma.”

11. Sai suka mai da hankali gare shi, don ya daɗe yana ta ba su al'ajabi da sihirinsa.

12. Amma da suka gaskata bisharar da Filibus ya yi a kan Mulkin Allah, da kuma sunan Yesu Almasihu, duka aka yi musu baftisma mata da maza.

13. Har Saminu da kansa ma ya ba da gaskiya, bayan an yi masa baftisma kuma ya manne wa Filibus. Ganin kuma ana yin mu'ujizai da manyan al'ajibai, ya yi mamaki ƙwarai.

Karanta cikakken babi A.m. 8