Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:7-14 Littafi Mai Tsarki (HAU)

7. ‘Har wa yau kuma,’ Allah ya ce, ‘Al'ummar da za su bauta wa, ni zan hukunta ta, bayan haka kuma za su fito su bauta mini a wannan wuri.’

8. Ya kuma yi masa alkawari game da kaciya. Ta haka, da Ibrahim ya haifi Ishaku, ya yi masa kaciya a rana ta takwas. Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi kakanninmu sha biyun nan.

9. “Kakannin nan kuwa, da yake suna kishin Yusufu, suka sayar da shi, aka kai shi Masar. Amma Allah na tare da shi,

10. ya kuma tsamo shi daga dukan wahala tasa, ya ba shi farin jini da hikima a gun Fir'auna, Sarkin Masar, shi kuwa ya naɗa shi mai mulkin Masar, ya kuma danƙa masa jama'ar gidansa duka.

11. To, sai wata yunwa ta auku a dukan ƙasar Masar da ta Kan'ana, game da matsananciyar wahala, har kakanninmu suka rasa abinci.

12. Amma da Yakubu ya ji akwai alkama a Masar, ya aiki kakanninmu tafiyar farko.

13. A tafiyarsu ta biyu Yusufu ya sanar da kansa ga 'yan'uwansa, asalinsa kuma ya sanu ga Fir'auna.

14. Sai Yusufu ya aika wa ubansa Yakubu yă zo, da kuma dukan 'yan'uwansa, mutum saba'in da biyar.

Karanta cikakken babi A.m. 7