Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:6-9 Littafi Mai Tsarki (HAU)

6. Abin da Allah ya faɗa kuwa shi ne zuriyar Ibrahim za su yi baƙunci a wata ƙasa, mutanen ƙasar kuwa za su bautar da su, su kuma gwada musu tasku har shekara arbaminya.

7. ‘Har wa yau kuma,’ Allah ya ce, ‘Al'ummar da za su bauta wa, ni zan hukunta ta, bayan haka kuma za su fito su bauta mini a wannan wuri.’

8. Ya kuma yi masa alkawari game da kaciya. Ta haka, da Ibrahim ya haifi Ishaku, ya yi masa kaciya a rana ta takwas. Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi kakanninmu sha biyun nan.

9. “Kakannin nan kuwa, da yake suna kishin Yusufu, suka sayar da shi, aka kai shi Masar. Amma Allah na tare da shi,

Karanta cikakken babi A.m. 7