Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:48-60 Littafi Mai Tsarki (HAU)

48. Duk da haka Maɗaukaki ba ya zama a gidaje, ginin mutum. Yadda Annabi Ishaya ya ce,

49. ‘Allah ya ce, Sama ita ce kursiyina,Ƙasa kuwa matashin ƙafata.Wane wuri kuma za ku gina mini?Ko kuwa wane wuri ne wurin hutuna?

50. Ba da ikona na halicci dukan waɗannan abubuwa ba?’

51. “Ku kangararru, masu ɓatan basira, masu kunnen ƙashi, kullum kuna yi wa Ruhu Mai Tsarki tsayayya. Yadda kakanninku suka yi, haka ku ma kuke yi.

52. A cikin annabawa wane ne kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun kuma kashe waɗanda suka yi faɗi a kan zuwan Mai Adalcin nan, wanda a yanzu kuka zama maciya amanarsa, da kuma makasansa,

53. ku ne kuwa kuka karɓi Shari'a ta wurin mala'iku, amma ba ku kiyaye ta ba!”

54. Da suka ji haka, suka husata ƙwarai da gaske, har suka ciji baki don jin haushinsa.

55. Amma Istifanas, a cike da Ruhu Mai Tsarki, sai ya zuba ido sama, ya ga ɗaukakar Allah, da kuma Yesu tsaye a dama ga Allah.

56. Sai ya ce, “Ga shi, ina ganin sama a buɗe, da kuma Ɗan Mutum tsaye dama ga Allah.”

57. Amma suka ɗauki ihu ƙwarai, suka tattoshe kunnuwansu, suka aukar masa da nufi ɗaya,

58. suka fitar da shi a bayan gari suka yi ta jifansa da dutse. Shaidu kuwa suka ajiye tufafinsu wurin wani saurayi, wai shi Shawulu.

59. Suna ta jifan Istifanas, shi kuwa yana ta addu'a, yana cewa, “Ya Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.”

60. Sa'an nan ya durƙusa, ya ɗaga murya da ƙarfi, ya ce, “Ya Ubangiji, kada ka ɗora musu wannan zunubi.” Da faɗar haka sai ya yi barci.

Karanta cikakken babi A.m. 7