Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:45-53 Littafi Mai Tsarki (HAU)

45. Alfarwan nan ita ce kakanninmu suka gāda, suka kuma kawo ƙasar nan a zamanin Joshuwa, bayan sun mallake ƙasar al'umman da Allah ya kora a gaban idonsu. Alfarwan nan kuwa tana nan har ya zuwa zamanin Dawuda,

46. wanda ya sami tagomashi wurin Allah, har ya nemi alfarmar yi wa Allahn Yakubu masujada.

47. Amma Sulemanu ne ya yi wa Allah gini.

48. Duk da haka Maɗaukaki ba ya zama a gidaje, ginin mutum. Yadda Annabi Ishaya ya ce,

49. ‘Allah ya ce, Sama ita ce kursiyina,Ƙasa kuwa matashin ƙafata.Wane wuri kuma za ku gina mini?Ko kuwa wane wuri ne wurin hutuna?

50. Ba da ikona na halicci dukan waɗannan abubuwa ba?’

51. “Ku kangararru, masu ɓatan basira, masu kunnen ƙashi, kullum kuna yi wa Ruhu Mai Tsarki tsayayya. Yadda kakanninku suka yi, haka ku ma kuke yi.

52. A cikin annabawa wane ne kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun kuma kashe waɗanda suka yi faɗi a kan zuwan Mai Adalcin nan, wanda a yanzu kuka zama maciya amanarsa, da kuma makasansa,

53. ku ne kuwa kuka karɓi Shari'a ta wurin mala'iku, amma ba ku kiyaye ta ba!”

Karanta cikakken babi A.m. 7