Tsohon Alkawari

Sabon Wasiya

A.m. 7:24-41 Littafi Mai Tsarki (HAU)

24. Da ya ga ana cutar ɗayansu, ya tare wanda ake wulakantawa, ya rama masa, ya buge Bamasaren, ya mutu.

25. Ya zaci 'yan'uwansa sun gane ta hannunsa ne Allah zai cece su. Amma ba su gane ba.

26. Kashegari kuma waɗansu suna faɗa, sai ya nemi shirya su, ya ce, ‘Ku jama'a, ku 'yan'uwa ne fa, don me kuke cutar juna?’

27. Amma mai cutar ɗan'uwa nasa ya ture Musa, ya ce, ‘Wa ya sa ka shugaba da alƙali a kanmu?

28. Wato kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe Bamasaren nan na jiya?’

29. Da jin wannan magana, Musa ya gudu ya yi baƙunci a ƙasar Madayana, inda ya haifi 'ya'ya biyu maza.

30. “To, bayan shekara arba'in, wani mala'ika ya bayyana a gare shi cikin harshen wuta, a wani kurmi a jejin Dutsen Sina'i.

31. Da Musa ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya matso domin ya duba, sai ya ji muryar Ubangiji ta ce,

32. ‘Ni ne Allahn kakanninka, Allahn Ibrahim da Ishaku da Yakubu.’ Sai jikin Musa ya ɗauki rawa, bai kuma iya ƙarfin halin dubawa ba.

33. Sai Ubangiji ya ce masa, ‘Tuɓe takalminka, domin wurin da kake tsayen nan, tsattsarka wuri ne.

34. Hakika, na ga wulakancin da ake yi wa mutanena da suke Masar, na ji nishinsu, na kuma sauko don in cece su. To, a yanzu sai ka zo in aike ka Masar.’

35. “To, shi Musan nan da suka ƙi, suna cewa, ‘Wa ya sa ka shugaba kuma alƙali?’ shi ne Allah ya aiko ya zama shugaba, da mai ceto, ta taimakon mala'ikan nan da ya bayyana a gare shi a cikin kurmin nan.

36. Shi ne kuwa ya fito da su, bayan ya yi abubuwan al'ajabi da mu'ujizai a ƙasar Masar, da Bahar Maliya, da kuma a cikin jeji, har shekara arba'in.

37. Wannan shi ne Musan da ya ce wa Isra'ilawa, ‘Allah zai tasar muku da wani annabi daga cikin 'yan'uwanku, kamar yadda ya tashe ni.’

38. Shi ne kuma wanda yake a cikin Ikkilisiyar nan a jeji tare da mala'ikan da ya yi masa magana a Dutsen Sinai, tare da kakanninmu kuma. Shi ne kuma ya karɓo rayayyiyar magana domin ya kawo mana.

39. Amma kakanninmu suka ƙi yi masa biyayya, suka ture shi, zuciya tasu ta koma ƙasar Masar.

40. Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana gumakan da za su yi mana jagaba, don Musan nan kam, da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya auku a gare shi ba.’

41. A lokacin nan suka ƙera ɗan maraƙi, suka yanka wa gunkin nan hadaya, suka riƙa farin ciki da aikin da suka yi da hannunsu.

Karanta cikakken babi A.m. 7